Download Yarima Ashman Chapter 7 & 8 Hausa Novel Complete PDF

YARIMA ASHMAN

Story & written by mmn fareesa

Chapter 7&8

Cigaban labarin

“”” bayan yasmeen ta idar da sallahne,suna zaune da Umma suna fira yah Omar yashigo d’akin,da sauri yasmeen ta tashi tana masa sannu da zuwa ta karbi ledar hannunsa.”

Budewa tayi ,murmushi tayi tace Yayana nid’aya nagode,zama yyi yana yar dariya yace baby (dayake haka yake kiranta)duk mijin da kka aura yabani da zaryan siyan fura any time.

“Keko gundurarki batayi?” Murmushi tayi tace ni bata wani gundurata wlh ,ko umma nah?

Girgiza kai umma tayi tace eh hakane tunkina karama kike sonta.

“Tashi tayi tace barama nadama abata,nan tafita tsakar gd”, umma takalli yah Omar tace ga abincinka nan!to yace had’e da jawo kular yyi bissimilla yafara ci,saiga yasmeen ta shigo da kwano da ludayi.zama tayi suna fira abin kwanin sha’awa,yah Omar be fitaba sai da aka kira isha’i.

**** **** *****

Washe gari byn yasmeen ta gama ayyukan gd ta shirya dan xuwa skul,tana fitowa dg gida yah Omar zai shiga nan tafara masa shagwaba adole saiyakaita skul.

” yar dariya yyi dan yah Omar akwai saukin kai yace to baby muje.”daa,kayan sana’ata zanfito dasu amma muje nakaiki,turo baki tayi,shikuwa gd yakoma yafito da mashin ta hau suka wuce skul.

“Yana ajeta ,kubra data hangosu da sauri ta nufosu dan jiya tunda yarima yatafi da yasmeen bata runtsaba.”

Kallan yah Omar tayi tagaidashi cikin sakin fuska ya amsa had’e da yiwa yasmeen bye bye yatafi abinsa.

“Kubra taja hannun ta tace my friend wai ina yarima yakaiki jiyane?”dan wlh banyi baccin kirkiba nayita addua ALLAH yasa kada yyi Repin dinki. wata doguwar tsuka yasmeen ta ja had’e da cewa ni wlh har ma na manta da wannan sarkin girman kan,nanta labartamata yadda sukayi dashi.

” ajiyar zuciya kubra tayi tace to Alhmdllh tunda baimiki komai ba, nima nayi tunanin bazai mikiba k’ila sbd gsky mutumin kirkine haka naji abakin jama ‘a.

“Yatsina fuska yasmeen ta yi tace can ta matsemasa”, amma nayi alk’awarin duk sadda Muka sake haduwa dashi saina masa rashin mutunci”wlh.”

Kubra tayi y’ar dariya tace hmmm kibidai ahankali wlh nidama yace yana sonki don zakuyi matukar dacewa da juna wlh,zaro ido yasmeen ta yi had’e da bankawa kubra harara tace ALLAH yakiyaye dan natsanesa wlhy kadama kisake wannan tunanin. ta fad’a rai bace, had’e da cewa ni ba sa’ar soyayyarsa bace!sbd ni talakace ba yar kowaba,kuma ko ba hakaba bazan soshiba,inkika sake mun irin wannan maganar to zamu rabu wlhy.

“dafa kafad’arta kubra tayi tace ALLAH yabaki hkuri ,ban fadaba dan inbata miki raiba ALLAH yahuci zuciyarki,nan taja hannun ta had’e da kara bata hkuri suka wuce dan daukar lectures.

___________________

da misalin karfe 12:30pm su yasmeen neda kubra zaune a cikin k’awayensu,bayan sunfito dg lecture. Sai fira suke kafin ashiga wata .

” kamar dg sama yasmeen ta ga bash gabanta ,yana wani cika yana batsewa.”

Sai wani cin magani yake shiga Wanda ake tsoro a skul din.

“3quarter ne da t shart ajikinsa yyi wani dan iskan aski,irin na tantiran yan duniya,cikin isa yakalli yasmeen sama da k’asa yace ke zo ina son magana da ke.

” banxa tayi dashi ta nunama batasan dashiba.”

Sukuwa k’awayen su jininsu akan akaifa yake kada bash yahad’a dasu dan sunsan bashshida mutumci ko kad’an.

“Koda yaga taki kulasa, cikin fushi yace ke dabbar inace?” ina miki magana zakimun banxa.afusace yasmeen ta tashi tsaye had’e da nuna sa da yatsa tace kai wawa Wanda baisan ciwon kansaba,me ruwanka danine?da har kake shiga rayuwata haka ajeni kayine da zaka kirani duk sadda katashi to ni yasmeen nafi karfin hakan ga kowane jaki kuma inason kas…..wani wawan mari bash yyiwa yasmeen har Saida tafad’i k’asa ta kife bakinta ya fashe ya na jini.

“Azuciye bash yyi kanta yana cewa yau zaki son koni wanene ,zaki gane gwamma kid’a da karatu dan ko wannan sakaran Omar din be isa ya kwaceki a hannunaba ni zakiyiwa rashin kunya ,yafad’a yana tunkararta,ji yyi an rik’e masa hannu wa ta baya….”

Yasmeen kuwa sbd galabaita kasa tashi tayi,jitayi ankama hannun ta and’agowa tana d’agowa wazata gani…?

Hmmm tosu wanene suka rik’ema bash hannuwa?

Shin wa yasmeen ta gani?

Domin jin amsar wannan tambaya muhadu a page nagaba…

Yawan comments yawan typing.

Leave a Comment

This site uses Akismet to reduce spam. Learn how your comment data is processed.