Download KURKUKUN ƘADDARA Hausa Novel Complete PDF

KURKUKUN ƘADDARA is a popular Hausa novel that tells the story of a young woman who is destined for prison. In this blog post, we will provide information on how to download the complete PDF version of KURKUKUN ƘADDARA Hausa Novel.

KURKUKUN ƘADDARA💋

E21
daga alkalamin Boss Bature, writer of Abban Sojoji🌹
“Wlh duk wanda ya kuskura ya ƙara ɗauramun alhakin ciwon danish, Sai na yi mashi jahilin Bugun da zai gaza ta shi” A harzuƙe ta yi maganar, nan da nan kowa yasha jinin jikin shi,
Murya na kerma azeeza tace”dan Allah kowa ya yi haƙuri, nidai bana son tashin hankali, tun da tsohuwa tace mana gobe zai dawo to mu haƙura muje mu kwanta mana”
Sai da batool ta lalla6a kowannan su kafin ta samu, Suka nufi gadajensu kowa ya haye sama ya kwanta
Ya rage saura angel kaɗai a tsaye tana binsu da kallo, Yayin da tunaninta gaba ɗaya yana akan Danish,
Gyaɗa kai tayi tare da juyawa ta koma saman gadonta, har dare ya tsala bata runtsa ba, Allah na gani ta damu da rashin danish acikin su, tana ji aranta kamar wani abun ne zai faru da shi, ko a wani hali yake a yanzu oho Allah wa’alamu,
Lokacin da kowannan su ya yi bacci, tana cikin saƙe saƙe acikin zuciyarta, tajiyo motsin mutun, da sauri ta ƙyalla idonta don taga wanene
Wannan mutumin ne me jajayen kaya har ƙasa, hannun shi ruƙe da kaskon turaren wuta, sai yawo yake yi acikin ɗakin su, yana tafiya yana karanto wasu ɗalasimai, hannun shi ɗaya ruƙe da kaskon turaren wutar ɗayan hannun kuma yana amfani da shi wurin kora hayaƙin zuwa kowani sashe na cikin ɗakin,
Mamaki ne ƙarara akan fuskar angel ga tsoro tana ji, da sauri ta ƙudundune cikin bargonta, ta sanya tafin hannayenta ta toshe hancinta da bakinta kamar yadda ta yi jiya. Aranta tace”Yau ma ya dawo kenan”
Ya jima acikin ɗakin nasu yana turara masu hayaƙin, kafin taji tsit alamar ya tafi, da sauri ta yaye bargon tana faman sauke ajiyar zuciya,
Saukowa ta yi daga saman gadon jikinta na kerma, hasken fitilun nan guda uku ne ya ɗan haskaka Cikin ɗakin, fitila ta ruƙo a hannunta tana haska wurin gadajensu,
Kamar yadda tabi kowanansu jiya har gadon shi ta tottofe shi da addu’a, haka yau ma tabi gadajen su ta yi masu addu’o’i,
A daidai bakin gadon danish ta tsaya tana kallon shimfiɗarshi, bakomai ya faɗo mata aranta ba face jiya da tazo yi ma shi addu’a, ya damƙo hannunta yayi tunanin wani mugun abunne take yi mashi, ɗan abunda ya faru jiya atsakaninsu ya tsaya mata arai, matsawa tayi zuwa gefen gadon ta tsugunna tare da leƙa ƙarƙashin gadon tana haskawa da fitila, ganin babu wuƙar anan, yasa tayi tunanin ɗaga katifarshi,
koda ta ɗaga ƙarƙashin Katifar bata samu wuƙar anan ba, ba ƙaramin takaici taji ba, taso ace Ta gano inda wuƙar take kota samu ta lalata glass ɗin dake ajikin windon toilet ɗinsu,
Allah kaɗai yasan inda ya jefa wuƙar, wata’ƙil ma, ya maida ma tsohowa ita, guntun tsoki taja, yanzu shikenan narasa damar da nake ita? Babu wani makami da zan iya yin amfani dashi wurin rotsa gilashin, kodai naje toilet ɗin In ƙara dubawa? tana yin wannan tunanin ta miƙe da sauri ta nufi Cikin toilet ɗin, Ta tura ƙopar ta shiga daga Ciki, tana haska ko’ina da fitilar hannunta,
Abu biyu ne Yazo mata aranta, na farko Bokitin da ke acikin toilet ɗinsu Na ƙarfe ne, Na biyu kuma wannan tukunyar fulawar dake ajiye Jikin bango, waswasi ta shiga yi kodai tayi amfani da bokitin? ƙwara shi akan tukunyar fulawar, saboda Zata Iya rugujewa azo kuma buƙata bata biya ba, Anyi asara kenan,
Bata kaiga yanke shawarar dame zata yi amfani ba, ba zato ba tsammani Taji saukar hannun Mutun saman kafadarta, awani irin Firgice tayi kwakkwaran juyi Ta daddage ta ɗaga fitilar hannunta zata kwaɗawa mutun daya dafa kafaɗarta, wani irin ihu batool tasaki a tsorace take faɗin”wayyo! Ke ni ce fa, batool ce,’
Nauyayoyar ajiyar zuciya angel ta sauke, Tare da janye fitilar, ta daidai ta natsuwarta, ba ƙaramin dariya batool ta bata ba, ganin yadda ta gigice,
“Allah ya taimake yau, da kin kwanta jinya,”
Dariya batool tayi”Kin ban tsoro me kike yi acikin toilet ne”?
“Ke zan tambaya, dama baki yi bacci ba,? Taya akai kika faɗo mun Cikin toilet batare da neman izni ba, yanzu da ace wani uzirin nake yi fa?
Hannu batool ta sanya tana sosa kai, tace”raina ya bani cewa ba abunda kike yi ne, shiyasa na shigo Ciki, Kuma na ganki Ɗazu zuƙunne agaban gadon Danish bansan me kikeyi ba, Amma ina hasashen wuƙar shi kika je nema halan”
Yatsina fuska angel tayi”I don’t know why kin sa mun ido, ” ta yi maganar da zolaya,
Batool tace”saboda na damu dake”
Ruƙo hannunta angel tayi tare da janta suka fito daga Cikin toilet ɗin, a bakin ƙopar fita daga area ɗin suka ɗan tsaya suna magana,
“Na duba ko’ina batool banga wuƙar ba, kodai ya maida ma tsohuwa ne?”
Girgiza kai batool ta yi “I don’t think so, nafi tunanin yayi mata wani mugun 6oyan ne, shiyasa na baki shawarar ki shirya dashi, Ku samu kusanci sosai, ta hakanne zaki samu damar sanin inda ya ajiye wuƙar,’
Tur6une fuska angel tayi”Anya zan samu yardar danish, Kin fa ce yana da wuyar yarda da mutane, balle ni kuma daya ɗaurawa karan tsana,”
“Ki jaraba ke dai, Danish yana da sauƙin kai sosai, ya danganta da yarda kika tafiyar dashi, amma wani hanzari ba gudu ba, har yau baki faɗa mini me zaki yi da wuƙar Ba!? I ave to know,’
Ta tsareta da ido tana jiran jin amsar da zata bata, ƴan kame kame angel ta shiga yi don batasan batool ta gane ainihin abunda zata aikata, tasan bazata bari ba, zata yi kokarin dakatar da ita ne
Ganin tana ƙoƙarin ƙara tambayarta yasa tayin saurin katse mata hanzarinta da cewa
“Ko kinsan akwai wani mutumi da ke zuwa ɗakin mu tsakar dare yana yawo da kaskon turaren wuta a hannunshi?
Tayi maganar a kokarin ta nata gusar mata da zancen wuƙa,
“Yaushe kika ganshi”? Angel tace”ko yau yazo, jiya ma na ganshi, idan yazo Sai yaita yin magana cikin wani irin yare mara daɗin ji, sannan yana bin kowani gado yana kora hayaƙin zuwa kowani sashe na ɗakin mu,”
Maimakon taga mamaki akan fuskar Batool, sai taga ta saki murmushi tare da cewa” kada ki damu kanki angel, tsohuwace ae kullum idan dare ya tsala sai ta shigo ɗakin mu, ta turara mana hayaƙin Kariya,”
Maimaitawa angel tayi’hayaƙin kariya kuma? Jinjina kai batool tayi eh, mun ta6a tambayarta hayaƙin menene tace mana hayaƙin kariya ne daga sharrin baƙaƙen aljanu domin kuwa akwai su acikin kurkukun nan, kuma hayaƙin yana da waraka acikin shi, shiyasa zaki ga ko ciwo bamu cika yi ba”
Angel tace”Ni a iya sani na, idan har za’a ba mutun kariya ba hayaƙi yakamata ayi mashi ba, addu’a ya kamata ayi ma shi, sam ni ban yarda cewa hayaƙin kariya bane, dole akwai wani 6oyayyan sirrin a tattare da shi,”
Kafin batool ta kuma cewa wani abu, suka jiyo sautin shessheƙar kuka daga can cikin ɗakin su,
“Wanene ke kuka”? Angel ce tayi tambayar tana kallon batool,
Batool tace “Muje mu duba, ina tunanin Aziza ce, “
da sauri suka fito daga area ɗin toilet, suka faɗo cikin ɗakin, haskata Angel ta yi da fitilar hannunta, a tsaye suka ganta tsakiyar ɗakin sai kuka take yi tana laluban hanya saboda lalurar da take fama da ita, ta makantar dare (nyctalopia) bata iya gani idan dare yayi, ko kuma idan babu wadataccen haske, haka suke fama da ita, in ta farka zata shiga Cikin toilet, sai ta dinga kuka tana ambaton sunayensu har sai wani ya farka acikinsu ya rakata,
Tun lokacin da angel tayi noticing lalurar yarinyar, sai da tayi ma batool magana ta tambayeta tun yaushe take fama da ita? Batool ta bata amsa da cewa”tsohuwa tace haka aka halicce ta, da zarar dare yayi ganin ta ya ke ɗauke wa, koda an kunna hasken fitila biji biji take gani” tun daga wannan lokacin angel take jin tsananin tausayinta, tana matuƙar jin yarinyar acikin zuciyarta,
Ƙarasawa suka yi inda aziza taka a tsaye Angel ta ruƙo hannunta,
“Its ok stop crying muna atare dake, Ina zaki je ne”?
Cikin shessheƙar kuka tace”Fitsari nake ji ya matse ni,”
Bari naje na rakata, takai ƙarshen maganar tare da ruƙo hannun azeeza, suka nufi toilet, gefen gado batool ta koma ta zauna tana jiran fitowarsu, badajimawa ba Angel ta fito hannunta ruƙe dana azeeza, har saman gadonta takaita sai da taga ta kwanta, ta janyo mata duvet ɗinta ta lullu6a mata shi saman jikinta, tana jiyo muryar azeeza ta cikin bargon tana faɗin”I luv u so much angel,” murmushi angel ta saki tare da cewa”Luv u too my sister, Allah ya kare mun ke, ki amsa da ameen” tana jiyo muryarta tana faɗin”Amen” ba ƙaramin daɗi taji ba, wuce wa tayi zuwa nata gadon ta haye ta zauna tare da jingina bayanta,
“Ba zaki kwanta ki yi bacci ba”? Batool ce ta yi mata tambayar,
“Zan kwanta, Ina yin addu’a ne ko baki gani ba” kallonta batool tayi ganin ta ɗaga hannayenta biyu sama tana magana cikin harshen da bata sani ba, da larabci take yin addu’ar,
“Nima kiyi mun addu’ar, inaso,”
Angel tace”Toh, ki kwanta kiyi bacci, zanyi maki addu’a,” amsa mata tayi da toh , kafin ta kwanta,
Bayan angel ta kammala yin addu’ar ta ta sauko daga saman gadonta, tabi kowani gado ta tottofe su da addu’a, bayan ta kammala ta koma saman nata bed ɗin ta kwanta,
Daƙyar ta samu bacci ya yi awon gaba da ita, har mafarkin danish sai da ta yi saboda ta sanya wa ranta shi sosai,
Slowly ta soma ƙoƙarin buɗe idanuwanta, dishi dishi ta dinga ganin mutane kewaye da gadonta, sanya cikin baƙaƙen kaya hannunsu zaƙo zaƙo da dogayen akaifu, Kowanne ya ɗaga gudumar dake hannunshi da niyar rotsa mata kanta, A gigice angel ta zabura tana faɗin”Innallallahi wa’inna ilaihirraji’un” sautin dariya taji ta ko’ina acikin kunnanta, hannu tasa ta murza idanuwanta, tare da ware su akan mutanan da take gani, Su batool ne a jere, Sun nannaɗe hannayen rigunansu, Sai faman haki suke yi suna nishi kamar waɗanda suka sha gudu
“angel tun ɗazu muke jira ki bamu wani training ɗin, duk mun iya wanda kika koya mana” rubina ce tayi maganar,
Nauyayyiyar ajiyar Zuciya angel ta sauke, Ashe idanuwanta badai dai suke nuna mata ba, tayi tunanin wasu shaiɗanun aljanune suka kawo mata ziyara,
“Ki tashi Muje mu motsa jikin mu atare” Acewar batool,
Muryarta a disashe tace”Kun takuramun, ba haka ake ta shin mutun daga bacci ba, duk kun tsoratar dani” taƙarasa maganar tana jifarsu da harara hada murguɗa masu baki, gaba ɗaya suka tuntsire da dariya,
Muryar javed taji yana faɗin”Zata taso ko sai munzo mun cuccu6eta”? ya yi maganar yana naɗe hannun rigarshi, ɗaya bayan ɗaya take kallon fuskokinsu, zufa sai tsastsafowa take yi daga jikin su,
Ba ƙaramin burgeta su kayi ba, fuskarta ɗauke da murmushi tace”me yayi zafi javed, yanzu zan taso amma fa saina fara shiga toilet, “
Har suna haɗa baki wurin cewa”To kiyi sauri ki fito, muna jiran ki,” ƙarasa janye bargon Jikinta tayi tare da saukowa daga saman gadon, Suka matsa mata hanya tabi ta wuce,
Walking slowly ta nufi ƙopar shiga makewayinsu, Harta ruƙe handle ɗin ƙopar da niyar ta buɗe sai kuma ta ɗan dakata tare da juyawa tana kallon Haris dake kwance daman gadonshi, idanuwanshi na fuskantar ceilling, da alamun damu atattare dashi, tasan bakomai ya jawo hakan ba, face rashin ɗan uwanshi danish don ta lura ba ƙaramin ƙaunarsa yake yi ba, Yau ce rana ta farka da tafara Jin tausayin haris, duk yabi ya ƙuntata kan shi saboda rashin danish, Allah sarki danish kowa Jikin nashi yake”?
Janye idanuwanta tayi daga kan haris ta mayar dasu kansu Parveen dake a tsastsaye, Tace”Har yanzu ba wani labari game da dawowar danish”?
Jinjina kai su kayi”eh, mu ma munyi expecting ɗin idan muka farka daga bacci zamu same shi kwance a cikin mu, ashe ba’a dawo mana da shi ba”
In brittle voice Azeeza tace”nadamu da rashin ɗan uwanmu, Jiya har mafarkin danish nayi, Allah yasa su dawo mana da shi, idan ba haka ba ni ko abinci bazan Iya ci ba” muryarta tamkar zata fashe da kuka,
Mubeen yace”nikaina daurewa kawai nake yi amma gaba ɗaya zuciyata a raunace take da rashin danish” yana rufe baki, Naufal yace”idan har jikin danish baiyi sauƙi ba, Zaiyi wuya su dawo mana da shi yau” zuciyarshi a karaye yae maganar,
“Ni abunda nake jima tsoro ma, kada a ƙi dawo mana dashi, kamar yarda ake yi mana a lokacin baya” Da sauri angel ta kalli fuskar batool da ta yi maganar, a yanayi na jin farga ba, tunawa tayi da tattaunawarsu da ita jiya a cikin toilet area, Inda batool take faɗa mata cewa”A lokacin baya duk wanda aka ɗauko acikinsu ba’a dawo dashi, He has gone forever,” da sauri ta shiga girgiza kai tana faɗin”that’s impossible, danish must be back, ku kwantar da hankalinku, babu abunda zai same shi, bana so inji kuna xancen cewa ba lallai danish ya dawo cikin mu ba, ‘ a harzuƙe takai ƙarshen maganar tare da buɗe ƙopar ta shige ciki, Koda ta shiga cikin toilet ɗin a jikin bango ta jingina bayanta, Idonta akan windown nan data kwallafawa ran son fasa ta,
“Da ace xan iya samun damar rotsa gilashin nan, dana yi ƙoƙarin binciko inda treatment room ɗin nan yake, kodan saboda inga danish, bawan Allah, ni tsorona ma kada ya rasa ranshi batare da ya kar6i kalmatusshahada ba, banaso ɗaya daga cikin su ya rasa ranshi batare da na musuluntar da shi ba, idan har hakan ta faru i won’t forgive my self, tabbas zanyi asarar jinkirin da nayi,’
cikin shessheƙar ku ka tayi maganar tuni hawaye sun soma sintiri akan fuskarta, ta ɗauki tsawn lokaci a tsaye batare da ta ta6uka komai ba, Har sai da tajiyo muryar Batul daga waje tana kwala mata kira”Angel! Angel! Kixo mu yi breakfast giants sun zo, ke kaɗai muke jira” Daƙyar ta iya ɗaga murya tace”Kada ku jira ni, ku fara kawai,”
Takai ƙarshen maganar tare da sanya hannayenta biyu Ta tu6e kayan jikinta asaman igiya ta ɗaura su, wanka ta samu tayi bayan takammmala ta mayar da kayan Jikinta,
Lokacin da ta fito daga Cikin toilet ɗin, A zazzaune ta same su saman red Carpet, a tsakiyarsu wooden trays ne na kayan abincinsu, kowa ya hallara banda mutun biyu ita da kuma Haris dake kwance yana kallon ceilling, yadda tabarshi haka ta same shi,
Ba irin lallashin da batool ba tayi mashi ba akan ya taso yaci abinci amma ya kafe akan sai an dawo mashi da ɗan uwanshi, a dole suka ƙyale shi,
A hankali angel ta ɗaura idanuwanta akan su giants dake a tsaye kamar gumaka sun goya hannayensu saman ƙirjinsu,
Maimakon taje ta zauna taci abincin, sai gani su kayi ta nufi Inda su giants suke a tsaye, A ruɗe batool ta shiga kiran sunanta tana faɗin”Angel where are u goinig? Ki zo muyi breakfast” ko kallon inda batool take ba tayi ba, Tana ƙarasawa gaban giants, taci burki ta tsaya tana ƙare masu kallo, ga tsoronsu tana ji haka nan ta daure ta cije, ganin kanta take yi wata ƴar ƙaramar halitta agabansu, saboda a Halittar jikinsu, Gabza gabza ne ga ƙirar jiki mai matuƙar razanarwa,
“Pls angel kada kija mana muna zaman lpy, ki dawo ki zauna acikin mu muci abinci” hanna ce tayi maganar,
Yasmin ma tace”Angel, giants basa ji basa gani, Kada ki ce zaki tanka masu, suna iya yi maki illa” Kowa yasha Jinin Jikin shi, duk tana sauraron magiyar da suke Yi mata, amma taƙi koda juyawa ta kalle su, hatta haris dake acan kwance saman gadonshi, Ganin angel agaban giants Yasa shi yin zumbur ya miƙe zaune yana kallon Ikon Allah, Azeeza har ta fara kuka saboda tsabar tsoron kada su cutar da angel,
Sai da angel ta gama kalle su daga ƙasa har sama, Kafin tace”Ko dabba idan a ka yi mata magana tana responding ballanta kuma ku da kuke Jinsin bil’adama, Meyasa a koda yaushe Kuke yin 6adda kama idan zaku zo wurin mu? Why? u can’t even talk to us? Saboda rashin gaskiya wato kuna tsoron muga fuskokin ku saboda gudun kada mu tona maku asiri nan gaba idan Allah ya ku6utar damu ko? Tayi tambayar cike da tuhuma tana kallon su, Ko motsi wannan ba suyi ba, Balle ma ta gane cewa suna sauraronta,
“Ko gunki bazai nuna maku yadda ake tsayuwa ba, agoya hannu saman ƙirji, ku dai ga ku nan wasu hamagawa da ku, to kodai ba mutane bane ku? Nafi zargin cewa ku ɗin Robot ne, wato sarrafa ku akeyi daga Can sama, ta yadda baku iya furta komai sai an baku izni koba haka ba”? Tayi tambayar a harzuƙe tana kallonsu,
Su batool sai faman lalla6a angel suke yi akan ta daina yi masu magana tazo suci abinci, amma ƴar tahalikar nan ko kallon inda su ke ba ta yi ba, sai ma cewa tayi”Su rabu da ita, Suci abincin su, Yau sai taga abunda ya turewa buzu naɗi, a tsakanin da giants dole suyi mata magana,
Atsiwace tace”Ba zakuyi mun magana ba? wlh duk ranar da wani ya kuskura acikin ku, Ya furta koda kalmar A ce, zan gano ko wanene shi koda bansan shi ba, idan har naji muryarshi awani wuri zan shaida shi ne, saboda Allah yayi mun baiwar tantance muryar mutane,” A zafafe takai karshen maganar, ga yunwa tana ji amma taƙi zuwa taje taci abinci,
Ruƙe qugu tayi”meyasa baku dawo mana da danish ɗin mu ba? ina kuka kai mana ɗan uwan mu? Tsohuwa tace kune kuka zo kuka ɗauke shi”? Tayi maganar tana faman haɗiyar yawu,
Aiki fa ya ga angel , ita kaɗai sai sambatu take yi kamar wata zautacciya,
Ganin taƙi zuwa taci abinci Yasa batool taje ƙarƙashin gadonta, ta ɗauko kwandonta, ta kwashe ragowar sauran abincin da suka Ci, da niyar ta ajiye ma angel da haris,
“Giants we are done,” Javed ne ya sanar dasu, yayi hakan ne don su samu su tafi, kafin angel takaiga ƙure su, don in suka fusata, komai zasu iya aikatawa,
Ta gefen angel suka bi suka wuce, Tattara kayan Abincin su kayi a jera suka nufi benan, Ganin zasu tafi basu bata amsar tambayarta ba, yasa ta watsa da gudu ta riga su hayewa saman benen, a jikin ƙofar ta jingina bayanta tare da ware hannyenta, wato ta toshe masu hanyar sa zasu bi su fuce,
Tsayawa su ka yi a tsaye saman matattakalar benan, tunda suke aiki a prison ɗin, basu ta6a ganin hatsabibiyar yarinya irin wannan da take agabansu ba, da ace tasan irin hatsarin dake gare su da bata yi gigin shiga huruminsu ba,
Kallon kallon aka soma Yi atsakaninta angel dasu giants, Hankalin su Batool yayi matuƙar tashi, duk suna a tsaye bakin benan sai roƙon angel su ke yi akan ta matsa ta basu hanya su wuce, ba iri magiyar da basuyi mata ba, amma angel ta maƙe kafaɗa akan bazata matsa ta basu hanya ba, Ita so take taga ikon Allah Shin giants zasu Yi mata magana akan ta basu hanya su wuce ko kuwa”?
Cikin muryar fushi haris Yace”wai ke baki da hankali ne? Ba zaki matsa ki basu wuri su wuce ba? an faɗa maki basa magana, idan ma abunda kike ma hari kenan,” rai a6ace tace”babu ruwan kowa dani, ku kama harkar gaban…….”
bata kai ƙarshen maganar ba, Taga ɗaya daga Cikin giants ɗin ya miƙa ma na gefenshi Kayan abincin dake a hannunshi, Ya kar6a ya haɗa dana hannunshi, Zuba ido tayi tana jira taga me zasu Yi mata, wani irin zazzafan taku giant ɗin yayi yadda kasan Zaki Ya nufi abun harinsa, tuni jikin angel ya soma kerma, ta ƙanƙame jikinta tana girgiza mashi kai, muryarta na kerme ta shiga faɗin”wlh kada ka kuskura ka ta6a…..”
(Wannan ne karo na ƙarshe da zanyi posting agrp dinnan, Saboda Baku Comment ba likes, Alamace dake nuna baku so, Don haka meson Cigaban Labri Yayi mun magna

KURKUKUN ƘADDARA💋

Dedicated to Aunty kubra

E28

Daga alƙalamin Boss Bature writer of Abban sojoji
Zuro ƙafarta ƙasa tayi daga saman gadon, ganin sun rufe idanuwansu yasa ta lalla6a cikin sanɗa taje gaban Carpet ta ɗauki fitila, da sauri ta wuce ta shiga sashen toilet ɗinsu, Taja ƙopa ta garƙame ta, ajiyar zuciya ta sauke yayin da bayanta ke ajingine da ƙopar,
Glass window ɗin ta ƙurawa ido daga inda take a tsaye, tana ƙoƙarin motsawa da nufin taje ta fara aiwatar da aikin fasa shi, kwatsam Tajiyo shessheƙar kuka tare da Iface iface daga Can Cikin ɗakinsu, A matuƙar kiɗime ta juya takai hannu ɗaya ta Zare jam lock ɗin kopar, da gudun gaske ta faɗo Cikin Ɗakin, Tunkafin ta ƙarasa Ciki, Ta hango su batool da hanna, agaban gadon Deeja, su javed kuma suna a tsaitsaye gaban gadon parveen, ga kuma haris da danish agaban gadon Rubina, Hankalinta yayi matuƙar tashi, Iskokai ne suka tashi Ko kuwa menene? Karasawa ciki ta yi da sauri taci burki agaban Gadon Parveen, Idonta akanta, Ta daddafe Cikinta sai juyi take yi tana kuka tana fadin Cikinta Ciwo zata mutu su taimaka mata,
Arude ta kalli fuskokinsu Batool, Bakomai ta gani ba face tsantsar tashin hankali, sun rasa ya zasu yi mata, da sauri angel ta matsa gadon Deeja dake ta ihu tana fadin Cikinta ciwo yake yi mata, wuce wa tayi zuwa gadon rubina ta tsaya tana kallonta itama ta daddafe Ciki sai kuka take yi tana matse idanuwanta, fuskarta tayi jaga jaga da kwalla,
Kallon Su haris Tayi muryarta na kerma tace”MEKE FARU WA NE’?_
Fuskar Haris a hargitse ya bata amsa da cewa”mu ma bamu sani ba, muna a kwance muka Ji sautin kukansu, mun rasa ya zamuyi da su”
Shiru angel ta ɗanyi ta ruɗe ta rasa madafa, Komawa Tayi bakin gadon Parveen, su batool duk suna a tsaitsaye cirko cirko, a ƙasa ta sauke fitilar hannunta, kafin ta ɗago takai hannu ta janyo Parveen zuwa Jikinta, ƙanƙameta praveen ta yi sosai tana kuka tana faɗin” angel ki taimaka mun ciki na, bana jin daɗi, xafi yake yi mini raɗaɗi nake ji,
Ƙura ido angel tayi tana kallon ɗigon Jinin dake ajikin wandon Parveen Nan take ta gane cewa Jinin al’ada ne, a karo na farko kenan da ta ta6a ganin sunyi jini, ta jima tana mamakin ya akai basu fara ba, saboda a shekarunsu ya isa ace sun fara Shi tuntuni saboda sun girmeta, abun ya ɗaure mata kai,’ shessheƙar kukan Parveen ne Ya dawo da ita Cikin hayyacin ta,
Ɗago da kanta tayi daga Jikinta, ta dafa kafaɗunta”Kiyi haƙuri kiyi shiru parveen zanje in faɗa ma tsohuwa,” takai ƙarshen maganar tare da saukowa daga saman gadon, ta kalli su batool dake atsaye Cikin yanayi na damuwa,
“Ku kula da su, Bari nayi mata magana tazo ta duba su, in yaso sai tayi maku bayanin Abunda ke damun su,” amsa mata su kayi da toh, da sauri ta nufi ƙopar ɗakin tsohuwa takai hannu ta bubbuga ƙopar, almost 3 times tana knocking ƙopar, Kafin tajiyo motsinta,
Buɗe ƙopar tayi tare da fitowa Hannunta ruƙe da sanda,
“Meke faruwa ne nake Jin koke koke” tayi tambayar tana kallon Wurin gadajensu,
Muryar angel na rawa ta bata amsa da cewa”ciwon Ciki suke yi Ina tunanin menstruation ne, suna buƙatar magani da kuma pads ɗin da zasu sanya”
Maimakon taga damuwa akan fuskar tsohuwa sai taga ta duƙar dakai ƙasa tana sakin wani irin shu’umin murmushi, ran angel ya 6aci sosai,
“Magana fa nake yi maki akan lalurar dake damunsu, don me xaki 6uge da yi mun murmushi? Maimakon Inga damuwa akan fuskarki? Kina ji suna kuka suna ihu amma ke ko ajikin ki? Ba zaki je ki duba lafiyar Jikin su ba”?
Ɗagowa tsohuwa tayi tare da kallonta, da wannan Shaƙaƙƙiyar muryartata ta tsoffi ta soma magana
“I ave no responsibility to check their health, the giants will come and take them to the treatment room” har saida angel ta zabura jin abunda tace, Can kuma ta wurga mata harara,
“Amma dai baki da Tausayi kuma baki da Imani, taya zaki ce za’a zo a ɗauke su? bayan kina da halin da zaki iya duba su da kanki? Kenan Giants su zasu duba Lafiyar su, Ke fa yakamata ace Kin duba su, Ba wani ƙato ba,” zuciyarta a harzuƙe takai ƙarshen maganar, Kafin tsohuwa ta mayar mata da martani, Suka Soma Jin motsi buɗe ƙopa daga can saman benan…………………….
A matuƙar kiɗime angel ta juya tana kallon stairs ɗin, hatta su Batool a ruɗe suka kai idanuwansu kan benan, tunkafin ma su ƙarasa saukowa sautin takalmansu ya karaɗe kunnuwansu, Cikin takun nan nasu na majiya ƙarfi suke tafiya bakowa bane face GIANTS, a jere suka sauko daga saman Stair cases ɗin, haƙiƙa hankalin angel yayi matuƙar ta shi, Jikinta har tsuma yake yi, juyawa tayi tare da kallon tsohuwa, Cikin karyayyiyar murya tace” na roƙe ki dan Allah Ki taimaka, kada ki bari a tafi dasu parveen, abar mana su acikin mu, Ni nayi alƙawarin zan kula dasu,” idanuwanta cike tab da ƙwalla takai ƙarshen maganar,
Girgiza kai tsohuwa ta yi babu alamun sassauci akan fuskarta tace”Ba hurumina bane shiga abunda ba ruwana, Dokar Prison ce, Wadda bani na tsarata ba, duk wani mara lafiya za’a zo a ɗauke shi akai shi inda za’a duba lafiyar shi, idan kinga na duba mutun to ciwon bai yi tsauri bane, Giants da ki ke gani basa sauraron kowa, Koda kuwa nice, saboda ba a ƙarƙashina suke ba, dukan mu Ma’akaita ne dake aiki gidan kurkukun ƙaddara, Kuma a ƙa’ida wani baya shiga hurumin wani………”
kalaman tsohuwa sunyi matuƙar girgiza angel, kafin ta yi yunƙurin buɗe baki ta furta wata kalma, tajiyo muryar parveen tana kuka tana faɗin Kada su bari a tafi da ita, mutuwa zata yi, ita bazata bi su ba ‘ a hargitse angel ta juya tana kallonsu, Kusan atare giants suka kai hannuwansu saman gadajensu Deeja da rubina da parveen, Wata irin ɗauka su kayi masu ta hanyar ruƙe waist ɗinsu suka yarfa su saman faffaɗan kafaɗunsu, bayin Allah Sai kuka suke Yi suna Bugun bayan giants da hannayen su, Nan take zuciyoyinsu Batool suka karaya Jikin kowan nan su yayi sanyi, har ma basu san lokacin da suka fashe da matsanancin kuka ba, Juyawa giants su kayi atare suka soma tafiya dasu ɗauke saman kafaɗunsu suka nufi stairs ɗin,
Da gudun gasken Angel ta tunkaresu Tana ƙarasawa bayansu Ta cafko hannayen parveen dake abayan giant ɗin dake ɗauke da ita, da iya ƙarfinta na ƙarshen ta janyota gaba ɗaya ta faɗo ta baya, baiwar Allah jikinta sai 6ari yake yi, ɗagowa tayi tare da rungume angel ta ƙanƙameta tana kuka tana faɗin”dan Allah angel kada ki bari su tafi dani, saboda basu dawowa da mu, bana so nabar Cikin ƴan uwana bansan inda zasu kai mu ba, Ina ji araina kamar na tafi kenan…….” Giant ɗin dake a ɗauke da Parveen Ya tsaya Tsak wanda ko ba’a faɗa maka ba, zaka shaida cewar A fusace yake, domin su ba’a katse masu aiki, Da gudun gaske su Hanna da su Javed suka ƙaraso Inda su angel ke a zaune ƙasa suna kuka,
Kallonsu kawai take yi idanuwanta sun rune ita kaɗai tasan irin tashin hankalin da take ci, Na raba ta da ƴan uwanta da ake ƙoƙarin yi,
Cikin shessheƙar kuka Batool tace” Dan Allah ki daina kuka Parveen, tsohuwa ta faɗa mana cewa Cuta ba mutuwa bace, Sai in kwanan mutun ya qare, Zasu yi maki magani ne zuwa gobe idan ku ka ji sauƙi zasu dawo mana da ku,” Ita kanta batool ta karaya sosai ta yi maganar ne kawai donta ƙarfafa mata gwiwa,
Zufa ta ko’ina Ajikin Parveen Muryarta na kerma tace”Koda ace ban dawo ba, Idan an kawo abinci, ku dinga ajiye mini nawa” Hawaye sharkaf akan fuskarta tayi maganar, angel dai takasa cewa komai, Zuciyarta ta gama karaya,
Kafin wani ya kuma cewa wani abu, Giant ɗin yakai Hannu da niyar ya ɗauki parveen, a tsorace ta ƙankame jikin angel tana faɗin” kada ki bari su tafi dani, bazasu dawo dani ba, idan har kuna sona dagaske ku taimake ni, kada ku bari araba ni daku……” ƙanƙameta angel tayi ajikinta, Giant ɗin ya damƙi qugun Parveen, ta ƙarfi ya fisgeta daga Jikin angel ya ɗaura ta saman kafadarshi Ya juya Cikin zafin nama Ya haura saman benan, Sauran Giants ɗin guda Biyu dake a ɗauke da rubina da Deeja suna abakin ƙofar fita suna jiran ƙarasowar shi, yana daga cikin dokar aikinsu Basa tafiya dole sai suna atare da juna, wani irin jiri ne Ya rufe idanuwan angel, anan ƙasa ta kwanta idanuwanta na zubar da hawaye, Suna Jiyo sautin muryar parveen cikin shessheƙar kuka take faɗin cewa”Angel dan Allah kiyi mini addu’a, Kuma idan gobe ba’a dawo dani ba, ku ajiye mini abinci na”
Wannan maganar ta parveen ta yi matuƙar kashe masu sassan Jikinsu, A nan suka wuni zuƙunne suna kuka, Mutun biyu ne acikinsu basu zubar da kwalla ba, Danish da Haris Saboda sun sa ma ransu cewa Za’a dawo masu da ƴan uwansu ne, duk da haka sun yi matuƙar damuwa da halin da su Parveen suka shiga, Na raɗaɗin ciwo ga kuma maraicin da zasu Yi na raba su da ƴan uwansu,
Tsohuwa dake a tsaye Bakin ƙopar ɗakinta, Ko a ha6ar xaninta bata sanya damuwar Halin da yaran suka shiga ba, Sai da taga Sun sassauta da yin kukan tukunna Ta dogara sanda ta nufi inda suke a zuƙunne ta tsaya tana kallon fuskokinsu da suka jiƙe sharkaf da hawaye
“Idan ku ka yi haƙuri, Za’a dawo maku da ƴan uwanku ne da zarar sun samu warakar Lalurar dake damun su, Kuka bazai ta6a yi maku maganin komai ba, Illa iyaka ya ƙara haddasa maku wata damuwar, Shawarar da zan baku shi ne, Ku sanyawa zuciyar ku haƙuri da juriyar rashin ƴan uwanku, kada ku cusawa kanku damu…….” bata ƙarasa maganar ba angel ta yunƙura ta miƙe zaune idanuwanta sunyi jawur gwanin ban tsoro, muryarta a zafafe ta soma magana
“Har kina da bakin zuwa ki bamu haƙuri akan mu yi shiru mu daina kuka? Wlh tun da nake 6anta6a ganin Muguwar mace azzaluma irinki ba!
Ɗan zaro ido tsohuwa tayi da kwala kwalan idanuwanta tamkar ƙwayar idanuwan zasu faɗo ƙasa,
“Kince ke uwa ce agare su, meyasa da naje na faɗa maki cewa Cikinsu na ciwo, baki zo kin duba jikin su ba? Koda sannu ne kiyi masu Amatsayinki na mahaifiyarsu, Amma bakiyi hakan ba, sai dai wasu ƙattai suka zo suka ɗauke su da sunan zasu duba lafiyarsu, bayan ke ya dace kiyi hakan a matsayinki na Ƴa mace, duk da bani da ilmi akan abun amma auntyna ta ta6a faɗa mini cewa Menstruation lalura ce ta mata da suke yi a kowani wata, zaki iya taimaka masu idan kinso basai an kaisu wani wuri ba……” cikin shessheƙar kuka takai ƙarshen maganar, Su batul duk sunyi zugudum suna sauraronsu,
“Banta6a jin tausayin wani ɗan adam ba aduniyar nan ba, kamar wadannan bayin Allah, wai su haka rayuwarsu zata ƙare? A tagayyare basu da me share masu hawayensu, basu da kafaɗar da zasu ɗaura kansu akai suyi kuka a lallashe su, Wannan wata irin Makauniyar ƙaddara ce? Tayi tambayar idonta akan tsohuwa dake a tsaye ruƙe da sanda, baka Iya gane awani hali take Ciki, domin kuwa fuskarta a haushine take, tsufanta da muninta sun ƙara bayyana
Juyawa tayi da sauri tana dogara sanda ta nufi ƙopar ɗakinta, tana ƙoƙarin kai hannu ta buɗe ƙopar muryar angel ta katse mata hanzarinta
“Ba zaki ce komai ba? Saboda rashin gaskiya? Zuciyarki ta bushe baki ji baki gani zalunci kaɗai kika sa agaba, wlh rantsuwar ɗan musulmi idan har ba’a dawo mana da ƴan uwanmu ba, SAI NA KASSARA RAYUWAKI, koda kuwa zan rasa raina ne’
Girgiza kai tsohuwa tayi batare data waiwayo ta kalleta ba ta soma magana
“Zaki Iya zagina ki ci mutuncina son ranki, saboda a yanzu ni kike ganin laifina, Unaisah ga shawara….” a ruɗe angel ke kallon bayan tsohuwa, Jin yau ta ambaci asalin sunanta,
Cigaba da magana tsohuwa tayi”ME ZAI HANA KIYI TUNANI AKAN WAƊANƊA SUKA SADAUKAR DAKU A GIDAN KURKUKIN ƘADDARA? mutun baya ta6a kasancewa acikin gidan kurkukun ƙaddara dole sai in Na JININSA NE YA SADAUKAR DASHI!!, nifa ba kowa bace agidan kurkukun nan face Ƴar Aiki me rainon Yara,” tsohuwa nakai karshen maganarta, ta yi saurin tura ƙofar ɗakinta ta shige taja ƙopa ta garƙame, ta tafi tabar angel da tunani, Zuciyarta ta shiga ruɗani, Kenan dama Tsohuwa bakowa bace Agidan kurkukun ƙaddara? Su kuma prisoners dake rayuwa acikinshi na Jininsu ne suka sadaukar dasu?tayaya kenan? Wata irin sadaukarwace wannan? Meyasa aka sadaukar dasu? Me za’ayi dasu? danginsu basa ƙaunarsu ne shiyasa suka sadaukar dasu ko kuwa?
Wani irin matsanancin ciwon kai ne Ya taso mata, me raɗaɗin gaske, da sauri ta sanya hannu ta dafe kanta, Ɗaƙyar ta iya ɗaga kafarta ta juya tana kallonsu Batul, waɗanda ke zazzaune Cikin jimamin rashin ƴan uwansu, da alama Basu ji komai ba game da abunda tsohuwa ta tattauna da angel,
“Wa suke dashi A duniyar nan? Zuciyarta ce ta bata amsa da cewa “ALLAH”
biji biji take gani acikin idanuwanta, daƙyar ta samu ta iya zuƙunna agabansu, Muryarta a disashe tace”kuyi haƙuri dare yayi sosai, Ku zo muje mu kwanta, ” miƙewa kowannansu Yayi, Suna jan ƙafa suka Nufi gadajensu Kowa Ya haye ya kwanta, sai da tabi su ɗaya bayan ɗaya tayi masu addu’a, taja masu bargunansu ta lullu6e masu Jikinsu, koda tazo saitin gadon Parveen sai da ta matse kwalla, bakomai take tunawa ba face kukan parveen da kuma kalamanta na karshe da take cewa Tayi mata addu’a kuma idan an kawo abinci su ajiye mata, angel tasha kuka kamar ba gobe, lokacin data zo kan gadon Deeja, tuni jikinta yayi sanyi tunawa da irin muguntar da tayi mata ɗazu da suna wasa, ta sanya gwiwar hannu ta daki bayanta harta kife ƙasa, cikin shessheƙar kuka angel ta furta “NAYI DANA SANI” Wuce wa tayi zuwa bakin gadon Rubina, Ta jima tana kallon shimfiɗarta, Kafin ta nufi gadonta ta hau sama ta zauna daga tsakiya, Hannayenta ta ɗaga sama Ta soma yi masu addu’o’i, Yayin da hawaye ke fita acikin idanuwanta, wasu na bin wasu,
A daren Ranar Kowa Ya runtsa banda Angel, Ta dage sai addu’a take yi masu ta hana idonta bacci duk don saboda su Parveen,
A washe garin ranar, dayawansu basu farka daga bacci ba, har lokacin tana a zaune tsakiyar gadonta, ta jingina bayanta jikin bango, fuskarta ta kumbura sumtun, tayi ja sosai, ga jirwayen hawaye,
Mutsu mutsun da taji ne yasa ta soma ƙoƙarin buɗe idanuwanta Sun kumbura ga raɗadi da suke yi mata, daƙyar ta samu ta ware idanuwan sosai, gefenta ta ɗan kalla don ganin wanene ya motsa, Danish ne ta gani zaune saman gadonshi, ya lumshe idanuwanshi fuskarshi babu alamun damuwa atattare da ita,
Zuro da ƙafafuwanta ƙasan gadon ta yi tare da gyara zama daga gefen gadon tana fuskantar danish,
Cikin sanyin murya ta ambaci sunan shi”Danish” a hankali ya buɗe idanuwanshi ya juyo yana fuskantarta,
“Ka tashi lafiya”? Jinjina mata kai yayi alamar eh, ajiyar zuciya ta ɗan sauke kafin tace” Inaso na tambaye ka wani abu idan ba damuwa” ya amsa mata da toh,
Saukowa tayi daga saman gadon, taje bakin gadonshi ta ɗan zuƙunna daga ƙasa, ta ɗago tana kallonshi idonsu acikin na juna tace
“Shekaran jiya da daddare, lokacin da na shiga cikin toilet ka biyo ni, Taya akai ka shigo bayan na datse ƙopa ta ciki na sanya jam lock”? ta tsare shi da ido tana jiran jin amsar da zai bata, ɗan tahalikin nan yayi shiru yana binta da ido batare daya motsa lips ɗinsa ba balle ma tayi tunanin zai bata amsa,
“Ba ka yi mini kama da maƙaryaci ba, duk da bana yarda da mutun ta yanayinsa, pls tell me the truth kawai inaso na sani ne, saboda kafin na shiga toilet ɗin sai da na tabbatar na barka a kwance kana bacci kafin na shiga ciki, Kuma ko bayan dana shiga saida na Haska ko’ina babu mutun, amma wani abun mamaki sai gaka acikin toilet ɗin, wanda nayi Imanin bata ainihin ƙopar ka shigo ba, Kuma baka Biyoni abaya ba” Cikin tuhuma take yi mashi maganar,
muryar shi a sanyaye yace” Bazan iya baki amsa ba, saboda ni kaina bansan ta ina na shiga ba, abunda na sani shine Na sanyawa raina inason nabi bayanki ne, kuma na samu kaina Acikin toilet ɗin shine kaɗai abunda zan Iya tunawa amma bayan wannan bansan komai ba”
Zuba mashi ido tayi tana kallonshi, har cikin ranta ta yarda da maganarshi, domin kuwa babu alamun wasa a fuskarshi ya bata amsar, kwara tabi komai asannu wurin yin bincike, Idan ba haka ba, zata iya tarwatsa lissafin kwakwalwarta ne,
Ƙaƙaro murmushi ta yi akan fuskarta, yayin da take kallon shi,
Mayar mata da martanin murmushin yayi Calmly yace” kin sanya damuwa aranki, Jiya kinyi kuka kuma baki yi bacci ba Why? Akan su Parveen ne”?
Jinjina mashi kai tayi alamar eh, ta ƙara da cewa”na damu dasu sosai, Ina ji araina kamar baza a dawo mana dasu ba, shiyasa zuciyata ta karaya har nagaza runtsawa”
Duƙowa taga ya yi saitin fuskarta, har saida ta ɗan tsorata, Zuciya da saƙe saƙe sai tayi tunanin ko kiss zaiyi mata, ƙiris ya rage tsinin hancinshi ya gogi nata, runtse ido tayi tana jin me zai mata
“Ki kwantar da hankalin ki, Zasu dawo na yi maki alƙwarin hakan,” ɗagowa tayi tare da kallon shi,
“Taya akai kasan cewa zasu dawo”? Tayi tambayar tana kallon cikin idanuwanshi,
Murmushin gefen fuska ya ɗanyi, Can kuma yace”Kin manta anzo an ɗauke ni, Kuma an dawo dani, Suma zasu dawo ne”
Girgiza kai angel tayi”amma koda aka dawo dakai, baka Acikin hayyacin ka, kamar an ƙara maka Ciwon Ajikin ka, danish zaka Iya tuna ina aka kai ka bayan an ɗauke ka daga Cikin mu”? ta jefa mashi tambayar,
“Angel, ba zan iya tuna komai ba, tun bayan da giants suka ɗauke ni bansan meya faru ba, har sai ranar da suka dawo dani cikinku tukunna na iya tuna wanene,”
Shiru angel ta yi bata kuma cewa komai ba, Lamarin ne yafi ƙarfin tunaninta, Wata irin Murɗaɗɗiyar sarƙaƙiyace Acikin Kurkukun mai wuyar fassaruwa,
Miƙa hannu danish yayi tare da ruƙo nata hannun acikin na shi, Magana ya soma yi idonshi acikin nata”angel, ina neman yafiyarki, for everything that happened because of our misunderstanding, I hate you for no reason, but now I can say that I love you more than anyone……..” kalaman shi ba ƙaramin sanyaya mata zuciya su ka yi ba, sai taji tamkar an yaye mata damuwarta na ɗan wani lokaci,
ƙayataccen murmushi ta saki tana motsa lips ɗinta, alamar tana so tace wani abu amma ta kasa furtawa, sam batayi tsammanin jin hakan daga gare shi ba, ta yi farin Ciki saboda yana ɗaya daga Cikin nasarar da take so ta samu na Jituwa atsakaninta da kowannan su, tana so ta shiga cikin zuciyoyinsu sosai ta yarda zata samu damar janyo ra’ayinsu, yanzu saura mutun biyu ya rage mata haris da deeja, taci alwashin Idan aka dawo da deeja bazata ƙara bari faɗa ya haɗa su ba, Shi ma haris ɗin bazata biye mashi ba, xata jasu ajikinta,
“What are u thinking about”? Jin voice ɗin danish yasa ta ɗanyi firgit ta kalle shi, still idanuwanshi na akan fuskarta,
” baki bani amsa ba,” ya tambaya yana sauraranta,
“Dama ni ban ruƙe ka azuciyata ba, Ni baka yi mini laifin komai ba, dani dakai tamkar ƴan uwana ne jini,” ba ƙaramin daɗin kalamanta yaji ba, har cikin zuciyarshi yaji sanyi, zame hannunshi yayi daga Cikin nata, ganin ya lumshe eyes ɗinshi yasa tayi tunanin ko bacci zai koma ne,
Yunƙurawa tayi tare da miƙewa daga gaban gadon shi, A dai dai Lokacin Batool ta fito daga sashen makewayinsu, itama fuskarta a kumbure, suna haɗa ido da angel ta nufeta, rungume juna su kayi kowa yayi shiru, batare da sunyi magana ba,
Azeeza dake zaune saman gadonta, farkawarta kenan idanuwanta na akansu,
Sun ɗauki lokaci kafin suka raba Jikinsu daga na Juna,”
“Idanuwanki sun nuna alamun baki yi bacci ba jiya, meyasa”? Batool ce tayi mata tambayar,
“Taya xan iya runtsawa, alhalin ƴan uwana suna Acikin mawuyacin hali, anzo an raba ni dasu, an kaisu wani wurin, dole na damu, Nayi kewarsu sosai, Na gaza jurewa ne…..” kukane ya ciyota, da sauri ta duƙar da kanta ƙasa, sam bataso ta nuna rauninta agabansu, saboda zata ƙara karya masu zuciya ne, sai dai duk ƙoƙarinta na hana kanta yin kukan hakann ya faskara, ita dai sam hankalinta bai kwanta da ɗaukar su parveen da akayi ba,
Dafa kafaɗunta Batool ta yi da hannayenta biyu, Cikin sigar lallashi tace”pls angel, u should stop shedding your tears, kina ƙara sanya mana damuwa ne, ke da kike ƙarfafa mana gwiwa yau ke ce da kanki ki ke zubar da hawaye to mu me zamu yi kenan”? Idon batul cike tab da kwalla tayi maganar,
Ta wutsiyar idonta ta hangi azeeza dake a zaune ta kasa kunne tana sauraronsu, da alama baccin bai sake ta ba, bata fahimtar me suke tattaunawa,
Sanin raunin azeeza yasa tayi saurin sanya tafukan hannayenta, ta share hawayen da suka wanke fuskarta, murmushi tayi wanda kai zuci ba takalli batool dake kallonta tace “Nadaina batool, bazan ƙara ba, kema kada kiyi kuka” jinjina kai batool tayi”Nima bazan bari hawaye na su zuba ba, Angel inaso mu haɗa hannu wurin taimaka ma sauran ƴan uwanmu, mu dinga lallashinsu muna basu baki har Allah yasa adawo dasu Parveen, Inaso mu sama ma junan mu farin ciki koda kuwa babu wani acikin mu, kamar ke da kika jure rayuwa batare da Mahaifinki ba, haka nakeso muma mu ƙarfafa zuciyoyin mu, mu yi rayuwa da sanin cewa wata rana samu iya rasa wani,
Ga Link na Tiktok Ɗina kuyi following dina, Zan yi posting na vedio din Prisners da kowa na kurkuku

Leave a Comment

This site uses Akismet to reduce spam. Learn how your comment data is processed.